in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta kudu tace rijiyoyin man kasar dake jahar Unity zasu dawo aiki
2017-01-06 09:49:27 cri
Kamfanin dillancin labarai na SUNA ya rawaito cewa, Sudan ta kudu ta sanar a jiya Alhamis cewar, rijiyoyin man kasar dake jahar Unity zasu cigaba da aiki nan da watanni biyu masu zuwa.

SUNA ya rawaito ministan albarkatun mai da iskar gas na kasar Sudan Mohamed Zayed Awad ya bayyana cewa a jiya Alhamis ya samu sako daga takwaransa na Sudan ta kudu Ezekiel Lol Gatkouth, inda ya bayyana masa cewa rijiyoyin man da aka dakatar da amfani da su a kasarsa za su dawo aiki cikin watanni biyu.

Ya jaddada cewa, an tanadi tsaro 100 bisa 100 don tabbatar da zaman lafiya a jahar ta Unity, ya kara da cewa, harma ya kai ziyarar aiki a inda rijiyoyin man suke a kwanakin baya.

A halin yanzu danyen man da Sudan ta kudun ke samarwa ya ragu da kashi 30 cikin 100, sakamakon barkewar tashin hankali tsakanin dakarun gwamnati da na 'yan tawaye dake yiwa tsohon shugaban kasar Riek Machar biyayya tun a watan Disambar 2013.

A baya dai kasar tana hako gangar danyen mai 245,000 a kullum, kafin barkewar tashin hankalin, kana daga bisani adadin ya ragu zuwa ganga 160,000 a kowace rana.

Rikicin na Sudan ta kudu yayi sanadiyyar hallaka rayukan dubban jama'a, kana ya tilasta mutane kimanin miliyan 1.9 tserewa daga gidajensu.(Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China