in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNMISS ya ce yana tattaunawa da gwamnatin kasar kan batun girke rundunar bada kariya.
2017-01-14 13:21:01 cri
A jiya Jumma'a ne shirin rundunar wanzar da zaman lafiya ta MDD a kasar Sudan ta kudu ta ba da sanarwa cewa, a yanzu haka, ta na tattaunawa da gwamnatin wucin gadi ta hadin kan al'ummar kasar, kan batutuwan da suka shafi girke rundunar sojin ba da kariya a kasar.

Sanarwar ta ce, rundunar ta lura da labarun da kafofin watsa labaru ke bayarwa, inda aka cewa, gwamnatin Sudan ta kudu na adawa da batun girke rundunar sojin.

Sanarwar ta ruwaito cewa, har zuwa yanzu, kasar na fuskantar tashe-tashen hankula, inda fararen hula da dama ke cikin matsalar rashin tsaro.

A ranar 11 ga wata ne, kakakin gwamnatin kasar Sudan ta Kudu Michael Makuei Lueth ya bayyanawa manema labaru cewa, an samu kyautatuwar tsaro a Juba, babban birnin kasar da yankunan dake kewayensa, a don haka, gwamnatin kasar ba za ta karbi shirin girke rundunar sojin ba da kariya a kasar ba. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China