in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shirin gina ci gaba na kasar Sin ya samu amincewar MDD
2017-02-12 12:03:34 cri
Wani jami'in diplomasiyya ya shedawa kamfanin dillancin labaran Xinhua cewa, shirin da gwamnatin Sin ta bullo da shi mai taken "raya cigaban bil adama" a jiya Jumma'a ya samu amincewa da goyon bayan daga MDD a karon farko, shirin ya kuma ja hankalin duniya baki daya.

A yayin zaman kwamitin raya cigaba na MDDr karo na 55, tuni kwamitin MDD ya cimma matsaya kan wannan shirin, sannan ya yi kira ga shirin raya cigaban da ya ba da fifiko ga ci gaban tattalin arzikin da zamantakewa a nahiyar Afrika.

A shekarar 2012 ne kasar Sin ta bullo da wannan shirin, da ma dai shiri ne dake da muradin bunkasa cigaban gwamnatoci na kasashen duniya, inda ya tanadi muhimman hanyoyi da kuma matakai da za su tabbatar da ingiza ci gaban duniya baki daya.

Jami'in diplomasiyyar ya ce, wannan shi ne karon farko da taron MDDr ya amince da wannan kuduri wanda kasar Sin ce ta bullo da shi.

Wannan mataki ya nuna a fili yadda mambobin MDD suka amince da wannan shiri na kasar Sin, wanda Sin ta daura aniyar tallafawa ci gaban gwamnatoci na kasashen duniya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China