in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kira taro don tattauna aikin asusun zaman lafiya da ci gaba tsakanin Sin da MDD
2017-02-04 11:24:39 cri
A jiya Jumma'a ne aka kira taron farko na kwamitin asusun zaman lafiya da ci gaba wanda kasar Sin da MDD suka kafa, taron da ya gudana a hedkwatar majalisar dake birnin New York.

Yayin taron, zaunannen wakilin kasar Sin a MDD mista Liu Jieyi ya ce, kafuwar asusun wani babban mataki ne da kasar Sin ta dauka da zummar zurfafa hadin gwiwa da MDD, kana wani mataki da kasar Sin ta dauka a ganin ta kara taimakawa majalisar baya, a kokarin da ta ke yi na tabbatar da zaman lafiya da cigaba a duniya.

Wakilin kasar ta Sin ya bayyana fatansa na ganin bangarorin Sin da MDD sun kara hada kai, don mai da asusun wani shahararren dandali ga hadin gwiwar bangarorin 2, tare da samar da gudummowa ga kokarin inganta ayyukan MDD, da raya harkokin da suka shafi bangarori daban daban na duniya, da wanzar da zaman lafiya da ci gaban duniya, gami da cimma burin daukacin dan Adam.

A nata bangare, Maria Viotti, darektan ofishin babban magatakardan MDD, ta ce majalisar tana godiya ga kasar Sin bisa tallafin da ta bayar cikin karamci. Ta kuma bayyana imani cewa, asusun zai taimakawa kokarin majalisar a fannonin kiyaye zaman lafiya da tsaro, da wanzar da samun ci gaba mai dorewa a duniya baki daya.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China