in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Adadin kudin haraji da yankin Tibet ke tattarawa ya karu a bara
2017-02-10 10:06:35 cri
Yankin Tibet dake kudu maso yammacin kasar Sin mai 'yancin cin gashin kai, ya ce ya samu karin kudin harajin da yake tattarawa da kashi 31.9 a cikin shekarar 2016, al'amarin da ya sanya yankin ya yi wa sauran yankunanan kasar Sin zarra a fagen samun bunkasar kudaden haraji cikin kankanin lokaci.

Ya kara da cewa ya samu wannan bunkasa ne ta harkokin kasuwanci, sufuri da kamfanonin fasahar zamani, amma ba ta kakabawa cinikayya haraji mai tsauri ba.

A cewar Hu Suhua, shugaban ofishin hukumar dake tattara haraji na yankin, habakar tattalin arzikin yankin ne ya kai shi ga samun karin kudaden haraji.

Hu Suhua ya kara da cewa, a cikin shekarar da ta gabata, ma'aunin tattalin arzikin yankin na GDP ya kai Yuan biliyan 114.8, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 16.5, inda ya ce ya karu da kashi 11.5 a kan na shekarar 2015.

Har ila yau, ya ce, shekaru ashirin da hudu a jere ke nan, da yankin ke samun bunkasar tattalin arzikinta a kowace shekara. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China