A jiya Jumma'a ne Alkalin kotun lardi a Amurka, James Robart ya yanke hukuncin da ya yi daidai da na wadanda atoney janar na jihohin Washington da Minnesota suka yanke, bisa wata karar da aka shigar gabansa da ke neman soke haramcin shiga Amurka da Shugaba Trump ya sanya.
Umarnin na Trump, ya haramtawa 'yan asalin wasu kasashe bakwai shiga Amurka.
Kasasehen sun hada da Iraqi da Syria da Iran da Libya da Somalia da Sudan da Yemen.
Wannan umarni dai na shan suka daga ciki da wajen kasar. (Fa'iza Mustapha)