in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta kulle kofa ga 'yan kasashen waje kimanin dubu 60
2017-02-04 10:17:18 cri
Will Cox, kakakin hukumar shigi da fici karkashin majalisar gudanarwar kasar Amurka, ya furta a jiya Jumma'a cewa, ya zuwa yanzu an soke takardun izinin shiga kasar kimanin dubu 60, kamar yadda shugaban kasar Donald Trump ya bayar da umarnin takaita shiga kasar.

Umarnin da shugaban ya gabatar a ranar 27 ga watan Janairu ya hana 'yan gudun hijira da wasu 'yan kasashe 7 a yammacin Asiya da arewacin Afirka shiga kasar ta Amurka. Wannan ya nuna cewa, Amurkar ba za ta karbi 'yan gudun hijira ba cikin kwanaki 120, kana an hana 'yan kasashen Iran, Sudan, Syria, Libiya, Somaliya, Yemen, da Iraki shiga kasar cikin kwanaki 90, haka kuma an hana 'yan gudun hijira na kasar Syria shiga cikin kasar Amurka ba tare da sanya wani wa'adi ba.

Bayan da shugaba Trump ya ba da wannan umarnin, Amurkawa suke ta sukarsa, tare da gudanar da zanga-zangar kin amincewa da wannan mataki, sa'an nan wasu kasashe da dama su ma sun bayyana ra'ayinsu game da kin yarda da wannan mataki na Trump.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China