in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara aiwatar da umurnin hana 'yan gudun hijira shiga kasar Amurka a filin jiragen saman Lebanon
2017-01-30 13:13:34 cri
A jiya Lahadi ne mahukuntan filin jiragen saman kasa da kasa na Beirut a kasar Lebanon suka fara aiwatar da manufar da kasar Amurka ta dauka ta hana dukkanin 'yan gudun hijira a duniya da ma 'yan kasashe 7 na yammacin Asiya da arewacin Afirka shiga kasar, inda aka haramta wasu fashinja da abin ya shafa shiga jiragen.

Kamfanin dillancin labarun kasar Lebanon ya bayyana cewa, an yi bincike mai tsanani kan dukkan jiragen sama da za su tashi zuwa Amurka a filin jiragen saman na Beirut, da kuma haramtawa fasinjojin dake dauke da Visan kasashen Syria, Iraki, Iran, Yemen, Libya, Sudan da kuma Somaliya shiga jiragen sama.

Wasu kafofin watsa labarum kasar ma sun ba da labarin cewa, a daren ranar 28 ga wata, filin jiragen sama na Paris na kasar Faransa, ya hana wani iyalin Syria da ya iso birnin daga Beirut zuwa birnin Atlanta na kasar Amurka, an kuma mayar da iyalin zuwa Lebanon. Daga baya, an fara aiwatar da wannan umurni a filin jiragen saman Beirut. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China