in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi tir da harin da aka kaiwa tawagar ta a kan iyakar Nijeriya da Kamaru
2017-02-02 12:01:23 cri
Shugaban ofishin MDD mai lura da yankunan yammacin Afirka da Sahel Mohamed Ibn Chambas, ya yi matukar Allah wadai da harin da aka kaiwa wata tawagar MDD a wani wuri dake kusa da kan iyakar Najeriya da kasar Kamaru, lamarin da ya sabbaba rasuwar mutane 5 tare da jikkatar wasu da dama.

Harin na jiya Labara dai ya auku ne lokacin da 'yan tawagar kwararru dake sanya ido kan wasu ayyukan musamman na majalissar, ke hanyar kauyen Hosere Jongbi, daura da Kontcha.

Da yake karin haske game da lamarin, kakakin MDDr Stephane Dujarric, ya ce tawagar na aiwatar da wani shiri ne da ya shafi yunkurin da ake yi, na kawo karshen takaddama kan wasu yankuna na iyakar kasashen Najeriya da Kamaru mai lakabin CNMC.

An dai kafa shirin CNMC bisa umarnin babbar kotun kasa da kasa, a wani mataki na samar da daidaito da tsaro a yankin.

Rahotanni sun nuna cewa kawo yanzu ba a tantance ko su wane ne suka kaddamar da wannan harin ba. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China