in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta tsawaita wa'adin aikin rundunar tabbatar da zaman lafiya a Afirka ta tsakiya
2016-07-27 10:48:20 cri
A jiya Talata, aka zartas da wani kuduri a kwamitin sulhu na MDD na tsawaita wa'adin aikin rundunar MDD dake tabbatar da zaman lafiya a Afirka ta tsakiya zuwa ranar 15 ga watan Nuwamban shekarar 2017.

Bisa wannan kudurin, adadin sojojin tabbatar da zaman lafiya na MDD ya kai dubu 10 da 750, tare da 'yan sanda 2080, kuma za su ci gaba da aikin sintiri. Muhimmin nauyin da aka dorawa rundunar shi ne, kiyaye fararen hula, da kare hakkin bil Adama, da samar da yanayin tsaro don aikin jigilar kayayyakin jin kai a kasar Afirka ta tsakiya.

Wannan kuduri ya kuma bayyana cewa, kwamitin sulhu na MDD yana maraba da Faustin-Archange Touadera da ya hau kan mukamin shugabantar kasar, da kuma kafa sabuwar gwamnatin kasar. Sannan ya nemi gwamnatin Afirka ta tsakiyar ta hanzarta samar da daidaito tsakaninta da bangarori daban daban na kasar, kuma ta girmama tsarin mulkin kasar da tabbatar da samun dauwamammen ci gaban kasar cikin lumana. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China