in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu ba da agaji na MDD na shirin kai tallafi Najeriya
2016-07-15 10:01:50 cri
Ofishin kula da jin kai na MDD (OCHA) ya fada a jiya Alhamis cewa, hukumomin ba da tallafi na MDD sun kammala shirye-shirye domin kai dauki ga mutane a kalla 275,000 wadanda suke rayuwa a sabbin sansanonin 'yan gudun hijira 15 wadanda ke karkashin kulawar sojoji a jihar Borno dake arewa maso gabashin Najertiya.

Kakakin MDD Stephane Dujarric, ya tabbatar da hakan ga manema labarai, ya kara da cewar hukumar na shirye-shiryen kai agaji a kan iyakokin Kamaru zuwa garin Banki dake Najeriyar, inda mutane 15,000 da rikici ya raba da muhallansu ke cikin halin matsananciyar bukata.

Ya ce hukumomin ba da agajin sun hada da asusun tallafawa kananan yara na MDD (UNICEF), da shirin samar da abinci na duniya (WFP), kuma tuni sun fara aiki da mahukuntan Najeriyar domin ba da taimako ga mutane 431,000, ciki har da samar da abinci mai gina jiki ga kananan yara.

Ya kara da cewa, hukumomin ba da agajin na bukatar kudi kimanin dala miliyan 221 domin samar da agaji kafin karshen watan Satumba a yankunan tafki Chadi da shiyyar arewa maso gabashin Najeriya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China