in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi Allah wadai da harin Mali
2016-11-08 09:39:04 cri
Kwamitin tsaron MDD ya yi Allah wadai da babbar murya, game da harin da aka kaddamar a tsakiyar kasar Mali wanda ya yi sanadiyyar kashe wani jami'in aikin wanzar da zaman lafiya, da fararen hula biyu.

A wata sanarwar da aka rabawa manema labarai, kwamitin majalisar dinkin duniyar ya bukaci gwamnatin kasar Mali da ta hanzarta gudanar da bincike domin gano wadanda suka aika wannan danyen aiki domin hukunta su.

Harin wanda ya faru a ranar Lahadi da ta gabata a kusa da Douentza a yankin Mopti dake tsakiyar Mali, ya yi sanadiyyar mutuwar 'yan kasar Mali biyu, da kuma jami'in wanzar da zaman lafiya guda, dan kasar Togo. Kana an jikkata wasu jami'an wanzar da zaman lafiyar 7, dake aiki karkashin tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD wato MINUSMA. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China