in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Ghana ya kara zabar wasu mutane da yake son nadawa ministoci
2017-01-25 09:26:07 cri

A jiya Talata, shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo, ya zabo karin mutane goma daga yankunan kasar daban-daban da yake son nadawa ministoci.

Idan majalisar dokokin kasar ta amince da nadin na su, za su yi aiki a matsayin wakilan shugaban kasa a yankuna goma dake kasar, inda tuni aka mika sunayensu ga majalisar don neman sahalewarta.

Yayin wani taron manema labarai, Akufo-Addo ya ce yana da tabbacin mutane da ya zaba, za su tabbatar da samar da nagartacciyar gwamnatin da ba a taba samun irinta ba a tarihin kasar.

Kawo yanzu, shugaban ya zabi mutane talatin da shida da yake son nadawa ministocin bangarori daban-daban, inda yanzu haka majalisar dokokin kasar ke aikin tantance su. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China