Ana dai zaton mutanen sun gamu da ajalinsu ne, sakamakon ayyukan masu fataucin mutane, kuma alamu na nuna cewa 'yan asalin arewacin Ghana ne dake yunkurin komawa gida daga tarayyar Najeriya.
Tuni dai aka mika gawawwakin mutanen zuwa dakin ajiye matattu dake garin Kara na kasar Togo, yayin da kuma 'yan sandan yankin suka bukaci 'yan asalin kasar Ghana mazauna yankunan Chereponi, da Bunkprugu, da Saboba, da su je garin na Kara domin duba wadannan gawawwaki, a wani mataki na yunkurin tantance su. (Saminu Hassan)