in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Ghana ya sanar da kashin farko na sunayen wadanda zai nada ministoci
2017-01-11 10:40:33 cri
Shugaban kasar Ghana Nana Addo Dankwa Akufo-Addo a jiya Talata ya gabatar da kashin farko na sunayen mutane 13, wadanda zai nada a mukaman ministoci ga majalisar dokokin kasar domin amincewa da su.

Shugaban kasar wanda ya sha rantsuwar kama aiki a ranar Asabar din da ta gabata, ya sanar da wannan mataki ne a lokacin taron manema labarai a fadar gwamnatin dake Accra.

Sunayen mutanen sun hada da wadanda suke da kwarewar aiki da kuma sabbi, cikin wadanda ke yin biyayya ga jamiyyar NPP, har ma da wadanda suka shiga jam'iyyar ba da jimawa ba.

Tsohon ministan kudi na kasar Yaw Osafo-Maafo, wanda ke jagorantar kwamitin shirye-shiryen mika mulki, an nada shi a matsayin babban minista wanda zai sa ido ga dukkan ministocin kasar.

Sabbin ministocin na dakon amincewar majalisar dokokin kasar ne bayan kwamitin majalisar ya kammala yin muhawara da kuma tantace su.

Shugaban kasar Akufo-Addo ya bukaci majalisar dokokin kasar da ta hanzarta amincewa da sunayen ministocin domin kafa gwamnati, don tunkarar dunbun matsalolin da kasar ke fuskanta, da kuma daukar matakan saukakawa game da wahalhalun da 'yan Ghana ke fama dashi. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China