in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Burundi ya ayyana ficewar dakarun kasar daga tawagar AMISOM
2017-01-17 19:28:59 cri
Mataimaki na farko na shugaban kasar Burundi Gaston Sindimwo, ya ce kasar sa ta umarci dakarun sojin ta, dake aiki karkashin tawagar wanzar da zaman lafiya a Somalia wato (AMISOM) da su janye daga tawagar.

Mr. Sindimwo ya ce hakan ya zama dole, duba da yadda ake kin biyan dakarun na Burundi kudaden alawus din su, alhali kuwa ana biyan takwarorin su na kasashen Uganda da Kenya. Ya ce ko shakka ba bu, ba wata kasa ta kirki da za ta lamunci irin wannan nuna wariya.

Mr. Sindimwo na wannan jawabi ne yayin wani taron mane ma labarai, inda ya kara da cewa, muddin kungiyar hadin kan Afirka ta AU ba za ta rika biyan dakarun kasar sa hakkin su yadda ya kamata ba, to kuwa mahukuntan Burundi za su umarce su, da su fice daga tawagar ta AMISOM tare da dukkanin kayan aikin su.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China