in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
GDP na Sin ya karu da kashi 6.7 bisa dari a shekarar 2016
2017-01-20 11:29:37 cri
Bisa labarin da hukumar kididdigar kasar Sin ta fitar a ranar 20 ga watan nan, an ce, ma'aunin tattalin arziki na GDP na kasar Sin a shekarar 2016 ya kai RMB biliyan 74412.7, adadin da ya karu da kashi 6.7 bisa dari idan aka kwatanta da na makamancin lokacin shekarar 2015.

Shugaban hukumar kididdigar kasa ta Sin Ning Jizhe ya bayyana cewa, a shekarar 2016, an fuskanci kalubaloli wajen raya tattalin arzikin kasa da kasa, sakamakon hakan, kasar Sin ta yi tsaiwa tsayin daka kan sabbin manufofinta na neman bunkasuwa, domin tinkarar kalubaloli yadda ya kamata, yayin da take kara karfin bunkasuwar zamantakewar al'ummar ta. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China