Jiya Talata, ma'aikatar tsaron kasar Mali ta ce, a wannan rana da sassafe, wasu dakarun da ba a san ko su wanene ba sun kai hari kan wani gidan kurkuku da ke birnin Niono da ke tsakiyar kasar, inda masu gadi 2 suka jikkata, yayin da wasu fursunoni 93 suka tsere.
Wani gidan telibijin mai zaman kansa a Mali ya labarta cewa, a wannan rana da karfe 2 na safe, wasu dakaru sun kai hari a gidan kurkukun, tare da 'yantar da dukkan fursunoni. Ya zuwa yanzu babu wata kungiya da ta yi shelar daukar alhakin kai harin. (Tasallah Yuan)