Amadou Haya Sanogo, shugaban juyin mulki na ranar 22 ga watan Maris din shekarar 2012, da ya sanya kasar Mali cikin rikicin siyasa da tsaro mai tsanani, ya dawo gaban fagen kasar dalilin shari'arsa da za a fara a wannan ranar Laraba a Sikasso mai nisan tazarar kilomita 380 daga Bamako, babban birnin kasar Mali. (Maman Ada)