in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyya mai mulki ta kasar Tanzania ta dora alhakin ikirarin da ake na karancin abinci a kasar kan jami'iyyun adawa
2017-01-18 11:10:22 cri
A jiya Talata ne Jam'iyya mai mulki a Tanzania CCM, ta soki jami'yyun adawa a kasar, da yunkurin sauya tunanin al'umma game da halin da abinci ke ciki a gabashin kasar.

Sakataren yada labaran Jam'iyyar Humphrey Polepole, ya ce 'yan siyasa da 'yan kasuwa, na ikirarin cewa ana fuskantar karancin abinci a kasar domin cimma muradinsu na kashin kai.

Ya shaidawa wani taron manema labarai a Dar es Salam, babban birnin kasar cewa, jam'iyyun adawa ne ke kirkiro matsalar na karancin abinci, domin taimaka musu cimma muradinsu na siyasa.

Polepole ya yi kira ga jama'a su yi watsi da bayanai marasa sahihanci da shugabannin adawa ke yadawa game da yanayin abinci.

Ya kuma yi kira gare su, su mara baya ga ayyukan da gwamnati take da nufin inganta walwalarsu da habaka tattalin arziki. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China