in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gudanar da taron baje kolin kayayyakin fasahohin noma a Tanzania
2016-12-27 10:02:47 cri
Birnin Arusha dake kasar Tanzania zai karbi bakuncin taron baje kolin kayayyakin fasahohin noma na shekara shekara dake gudana a kasar. A bana za a gudanar da taron ne tsakanin ranekun 26 zuwa 27 ga watan Janairun dake tafe.

Mashirya taron sun bayyana cewa, ana sa ran zai hada sassan jami'ai, da manoma, da kungiyoyin manoma, da kungiyoyi masu zaman kansu, da masu bincike. Sauran sun hada da 'yan kasuwa da masu zuba jari, da kuma bankuna.

Da yake tsokaci game da tasirin wannan taro, jami'in mai ba da shawarwari game da tsara manufofin inganta cinikayyar albarkatun gona, a ma'aikatar noma, da kiwo da kiwon kifi a Tanzania David Nyange, ya ce fasahohin da za a baje kolin su, za su taka muhimmiyar rawa, wajen zamanintar da cinikayyar albarkatun noma.

An dai fara gudanar da wannan baje koli ne shekaru 3 da suka gabata a birnin Chisamba, cibiyar noma ta kasar, bikin da tun daga wancan lokaci ya bude sabon shafi, a fannin bunkasa cinikayyar fasahohin noma da kiwo a daukacin bangarorin kasar. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China