in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
NAPTIP ta ceto mutane 459 a shekarar 2016
2017-01-18 10:59:17 cri
Hukumar da ke yaki da masu safarar bil-Adama a Najeriya (NAPTIP) ta ce ta ceto mutane 459 daga hannun masu aikata wannan danyen aikin a shekarar 2016 data gabata.

Kwamandan hukumar mai kula da shiyyar arewa maso yammacin Najeriya Shehu Umar ya shaidawa manema labarai cewa, daga cikin wannan adadi 187 maza, kana 272 kuma mata.

Ya ce, a wannan shekarar da muke ciki, hukumar ta fara ilimantar da jama'a game da illolin safarar mutane gami da matakan yadda za su kare kansu daga fadawa wannan tarko.

Kwamandan ya ce, rashin kudi, ita ce babbar matsalar da hukumar ta fuskanta a shekarar da ta gabata. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China