in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Buhari ya bayyana rashin jin dadinsa game da harin da aka kaiwa sansanin 'yan gudun hijira
2017-01-18 09:26:00 cri

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana takaicinsa dangane da luguden wuta bisa kuskure da sojojin saman kasar suka yi jiya Talata a kan wani sansanin 'yan gudun hijira na garin Rann a yankin Kala Balge na jihar Borno da ke yankin arewa maso gabashin kasar.

Kwamandan dakarun da ke yaki da mayakan Boko Haram a jihar ta Borno Lucky Irabor ya shaidawa manema labarai cewa, kimanin mutane 100 ne suka mutu ciki har da sojoji 2, da ma'aikatan bayar da agaji 2 baya ga wasu fafaren hula da dama da suka jikkata.

Ya ce, lamarin ya faru ne bayan da dakarun saman kasar suka samu bayanan asiri cewa mayakan Boko Haram suna kokarin sake hallara a yankin.

Tuni dai rundunar sojojin saman kasar ta tura jirgi mai saukar ungulu zuwa wurin da lamarin ya faru don kwashe mutanen da suka ji rauni. A hannu guda kuma gwamnatin jihar Borno ta umarci dukkan asibitocin gwamnati da ke yankin da su samar da magani kyauta ga mutanen da suka jikkata sanadiyar wannan hari.

Shugaba Buhari ya yi alkawarin taimakawa gwamnatin jihar Borno don kula da wadanda wannan hari bisa kuskure ya rutsa da su. Haka kuma ya bukaci jama'a da su kwantar da hankalinsu, duba da yadda dakarun kasar ke daf da kawar da mayakan Boko Haram a yankin arewa maso gabashin kasar baki daya. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China