A jiya Laraba gwamnatin Najeriya ta amince da baiwa baki 'yan kasashe waje 335 da suka nemi izinin zama a kasar yayin da ta yi watsi da bukatun wasu 165 na neman gindin zama a kasar.
Minsitan cikin gida na Najeriyar Abudulrahman Dambazau, ya shedawa 'yan jaridu bayan kammala taron majalisar zartaswar kasar a Abuja fadar mulkin kasar.
Dambazau ya ce kwamitin ministoci dake kula da bada shedar zama dan kasa, sama da mutane 500 ne suka mika bukatun neman izinin zama a kasar. Kuma daga cikinsu gwamnatin kasar ta amince da baiwa mutane 335 wadanda suka cika ka'idar samun izinin zama a kasar.(Ahmad Fagam)