in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi kira a kaucewa dagula batun Falasdinu da Isra'ila
2017-01-16 13:32:54 cri
A jiya Lahadi, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Zhang Ming, ya zanta da 'yan jaridun kamfanin dillancin labaran Sin Xin Hua a birnin Paris, inda ya ce, batun Kudus, wani batu ne mai sarkakkiya a rikicin Falasdinu da Isra'ila. Don haka kasar Sin ke fatan bangarorin masu ruwa da tsaki, za su yi kokarin shimfida zaman lafiya tsakanin Falasdinu da Isra'ila bisa adalci, kuma su kaucewa matakai da ka iya kara dagula batun.

An gudanar da taron wanzar da zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya bisa tayin kasar Faransa, taron da ya guda ranar 15 ga wata a birnin Paris, inda wakilai daga kasashe gami da kungiyoyin kasa da kasa kimanin 70 suka halarta, ciki har da kasar Sin.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China