in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yabwa Nijeriya kan martaba manufar kasar Sin daya tak
2017-01-12 20:00:44 cri
A yau Alhamis ne, kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin, Lu Kang ya bayyana a gun taron manema labaru cewa, Sin ta nuna amincewa tare yabawa Nijeriya matuka dangane da yadda ta tsaya ga martaba manufar kasar Sin daya tak a duniya.

Lu ya bayyana cewa, a kwanan baya, gwamnatin Nijeriya ta yanke shawara a siyasance kan harkokin da suka saba wa manufar kasar Sin daya tak da hukumomin yankin Taiwan a kasar suka yi, tare kuma da daukar matakai. A wata sanarwar hadin gwiwa da ministocin harkokin wajen kasashen biyu suka fitar a jiya Laraba, gwamnatin Nijeriya ta nanata cewa, manufar kasar Sin daya tak ta zama babban tushe na kafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare tsare tsakaninta da Sin.

Dadin dadawa, Lu ya furta cewa, Sin ta nuna amincewa da babban yabo ga Nijeriya wajen martaba manufar kasar Sin daya tak. Kuma wannan ya sake nuna cewa, wannan manufa ta sami amincewa da karbuwa ga kowa da kowa.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China