in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A Nijeriya, za a gudanar da bincike don gano inda kungiyar Boko Haram ke samun na'urar kirga lokaci da take amfani da ita don hada bam
2017-01-11 09:29:12 cri
A jiya Talata ne jami'an tsaro a Nijeriya, suka ce sun fara binciken inda kungiyar Boko Haram ke samun na'urar kirga lokaci da take amfani da ita wajen hada bam.

Ofishin hukumar tsaro da wanzar da zaman lafiya da aka fi sani da Civil Defence, dake jihar Borno a yankin arewa maso gabashin kasar, ya ce an kaddamar da binciken ne bayan gano cewa, mayakan boko haram sun yi amfani da bam da ake kayyade masa lokacin tashi a hare-haren da suka kai ranar Lahadin da ta gabata a babban birnin jihar wato Maiduguri.

Hukumar Civil Defence ta ce irin na'urar kirga lokaci, na ba masu kai hari damar sanin lokacin da bam din zai tashi.

Shugaban ofishin hukumar Civil Defence na jihar Borno, Ibrahim Abdullahi ya ce tun da yanzu an gano irin na'urar da 'yan tada kayar baya ke amfani da ita, to za su bi diddigi don gano daga inda suke samu.

Nijeriya ta samu nasara kwarai a yakin da take da kungiyar Boko Haram, inda jami'an tsaron kasar da ke yankin arewa maso gabas da ayyukan na Boko Haram ya fi kamari, suka karya lagonsu, ta hanyar fattatakar daga tungarsu dake dajin sambisa. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China