Yayin wani taron manema labarai da ya yi a fadarsa, Akufo-Addo ya sanar da nadin Akosua Frema Opare-Osai a matsayin shugabar ma'aikatan ofishin Shugaban Kasa.
Opare Osei ta kasance mace ta farko da za ta rike wannan mukami a kasar tun shekarar 1992
Haka zalika, zababben shugaban, ya nada Albert Kan Dapaah, tsohon Ministan harkokin cikin gida karkashin shugabancin John Agyekum Kufuor, a matsayin ministan tsaron kasar.
Yayin wani biki da za a yi a ranar Asabar a birnin Accra ne za a rantsar da shugaba Akufo-Addo. ( Fa'iza Mustapha)