in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana shirin zaben sabon kakakin majalisar dokokin kasar Ghana
2016-12-20 09:27:11 cri
A jiya Litinin ne majalisar dokokin kasar Ghana ta fara rajistar sabbin 'yan majalisun dokokin 275 da aka zaba, a wani mataki na zaben sabon kakakin majalisar da sauran jami'an da za su ja ragamar harkokin majalisar.

Wannan mataki na zuwa ne gabanin rantsar da shugaban kasar da aka zaba Nana Akufo Addo da za a yi a watan Janairun shekarar 2017.

Bisa kundin tsarin mulkin kasar ta Ghana dai shugaban kasar ne zai gabatar da sunayen mutane biyu da za a zaba a mukamin kakakin majalisa da kuma mataimakin kakakin majalisa na daya, yayin da ita kuma jam'iyyar NDC ta marasa rinjaye za ta zabi wanda zai rike mukamin mukaddashin kakakin majalisa.

Kwarya-kwaryar sakamakon zaben 'yan majalisun da aka fitar ya nuna cewa, jam'iyyar NPP ta lashe kujeru 170 yayin da NDC ta lashe 105. Gabanin zaben dai NDC ce ta ke kujeru 148 cikin 275 na majalisar. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China