in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bayyana Fadar Shugaban Kasar Najeriya a matsayin mai cike da tsaro
2017-01-07 12:00:49 cri
A jiya Jumma'a ne Hadimin Shugaban Najeriya ya ce fadar Shugaban kasar dake Abuja, babban birnin kasar, na cike da tsaro ga dukkan al'ummar kasar da kuma baki 'yan kasar waje.

Mataimakin Shugaban kasar na musamman kan harkokin yada labarai, Malam Garba Shehu ne ya bayyana tabbaci cikin wata sanarwar da ya fitar, bayan wani al'amari da ya auku a fadar ranar Laraba, inda aka samu kuskuren sakin kunamar bindiga.

Ya ce al'amarin ya auku ne bayan bindigar pistol na wani da ya kai ziyara fadar, ya saki kuna bisa kuskure a lokacin da yake mika bindigar a bakin kofa kafin shiga fadar.

Mutumin wanda jami'in tsaro ne, ya kai ziyara fadar ne bisa gayyatar da aka masa, a matsayinsa na shaida kan wani bincike da ake gudanarwa. Jami'in dai ba ya cikin jami'an tsaro da aka girke a fadar Shugaban Kasar. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China