in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun rundunar Sojin Nijeriya, sun kashe wasu mata 'yan kunar bakin wake uku.
2017-01-05 10:09:50 cri
Wani jami'in rundunar sojin Nijeriya ya ce dakarun da ke yaki da 'yan kungiyar Boko Haram a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar, sun hallaka wasu mata uku 'yan kunar bakin wake, a lokacin da suka yi kokarin kai musu hari a yankin Dutse dake karamar Hukumar Gwoza ta Jihar.

Kwamandan rundunar Operation Lafiya Dole, Manjo.- Janar Lucky Irabor, ya shaidawa manema labarai a birnin Maiduguri cewa, an yi nasarar kama 'yan kunar bakin waken ne bisa rahoton sirri da suka samu.

Ya ce, sun kama 'yan kunar bakin wake, sai dai uku daga cikinsu sun tirje, inda suka yi kokarin kutsawa cikinsu, yana mai cewa basu da wata mafia da ta wuce bude musu wuta.

Manjo Janar Lucky Irabor ya kara da cewa, dakarun Nijeriya da takwarorinsu na Kamaru, na samun nasara a kokarin da suke na kwato yankunan da ke kusa da Kauyen Ngoshe da Dutsen Gwoza, inda ya ce yayin aikin, sun samu makamai da alburusai da dama.

Har ila yau, ya ce sun yi nasarar cafke wani daga cikin 'ya'yan kungiyar, mai lamba 164 cikin jerin 'ya'yan kungiyar da rundunar soji ta ayyana nemansu ruwa a jallo.

A wani labarin kuma, Manjo Janar Lucky Irabor ya tabbatar da batun kama shugaban Karamar Hukumar Mafa ta jihar Borno Shettima Lawal, wanda ake zargin na da alaka da kungiyar ta Boko Haram.( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China