in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Nijeriya ya yi maraba da gano daya daga cikin 'yan matan Sakandaren Chibok
2017-01-07 11:33:47 cri
Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, ya yi maraba da batun gano Rakiya Abubakar, daya daga cikin 'yan matan nan na Chibok, a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar.

Shugaban kasar ya ce, gano yarinyar ya kara kyautata fatan da ake da shi na wata rana za a kai ga gano sauran 'yan matan tare da sada su da iyalansu, kawaye da kuma al'ummominsu.

Ya kuma yabawa rundunar sojin kasar bisa dukufa da ta yi da binciken da ya kai ga gano Rakiya, yana mai bukatar dakarun su ci gaba da irin jajircewar da ya kai su ga fattatakar 'yan ta da kayar baya daga dajin Sambisa.

Buhari ya kuma tabbatar da kudurin gwamnatinsa, na ci gaba da taimakawa rundunar soji da duk abun da take da shi, wajen gano sauran 'yan matan tare da fattatakar matsalar ta'addanci a Najeriya.

Wannan al'amari na zuwa ne bayan an saki 'yan matan Chibok 21 a watan Oktoban da ya gabata, bayan an cimma yarjejeniya da wadanda suka sace su. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China