in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Buhari: Najeriya za ta bunkasa sha'anin noma a sabuwar shekarar 2017
2017-01-02 12:10:11 cri
Shugaban Muhammadu Buhari na Najeriya, ya alkawarta daukar karin matakai, wadanda za su sauya akalar tattalin arzikin kasar daga kasa mai dogaro da cinikayyar mai da iskar gas, ya zuwa sha'anin noma da kiwo a cikin wannan sabuwar shekara ta 2017.

Shugaba Buhari wanda ya bayyana hakan cikin sakonsa na murnar shiga sabuwar shekara a jiya Lahadi, ya ce gwamnatinsa za ta kara kaimi wajen samar da guraben ayyukan yi, da yaki da cin hanci da rashawa, yana mai cewa nasarorin da gwamnatin tasa ta cimma ya zuwa wannan lokaci, sun karfafa masa gwiwa matuka.

Ya ce tuni aka fara sauya tsarin noma a sassan kasar daban daban, wanda hakan ya haifar da samun yabanya mai tarin yawa a shekarar 2016 da ta gabata, yayin da a hannu guda jahohin kasar ke da kokarin yin hadin gwiwa da sauran masu ruwa da tsaki wajen bunkasa noman shinkafa.

Shugaba Buhari ya kara da cewa lokacin dogaro kan albarkatun mai domin samun kudaden musaya na ketare na gushewa, kuma nan gaba kadan cikin wannan shekara, al'ummar Najeriya za su kara amfana daga nasarorin da gwamnatinsa ke samu a fannonin raya kasa daban daban.

Kaza lika ya yi kira ga 'yan Najeriya da su hada kai da juna, yana mai tabbatar da cewa wahalhalun da ake fama da su yanzu haka na daf da zama tarihi. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China