in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya: Za a mika mulki a Gambia lami lafiya
2017-01-05 10:58:27 cri
Ministan harkokin kasashen wajen na Najeriya Geoffrey Onyeama, ya bayyana tabbacin cewa, shugaba Yahya Jammeh na Gambia zai mika mulkin ba tare da wata matsala ba.

Minista Onyeama wanda ya bayyana hakan a Abujar, fadar mulkin Najeriya, ya ce shugaba Jammeh zai martaba muradun al'ummarsa da kiraye-kirayen da kungiyoyi da sauran kasashen duniya ke yi masa na ganin an warware takaddar siyasar kasar, duk da matsayin da ya dauka na kin amincewa da sakamakon zaben wanda tun farko ya amsa shan kaye.

Ya ce, Najeriya a nata bangaren za ta ba da gudummawar da ta dace na ganin an kawo karshen matsalar siyasar cikin ruwan sanyi.

Shugaba Jammey dai ya sha kaye a hannun Adama Barrow ne a zaben shugabancin kasar da ya aka gudanar . (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China