in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sudan ya kara wa'adin tsagaita bude wuta da wata guda
2017-01-02 12:17:00 cri
Shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir ya kara wa'adin tsagaita bude wuta da wata guda a dukkan yankunan kasar da ake fama da rikici. Shugaba al-Bashir ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi yayin bikin cikar kasar shekaru 61 da samun 'yancin kai. Ya ce, an dauki wannan mataki ne ba wai don kare kai ba.

Shugaban na Sudan ya kuma yi kira ga dukkan bangarori da suka yi watsi da shirin sasantawa na kasar, da su martaba kundin da taron sasantawa na kasar ya amince da shi a watan Oktoban da ya gabata. Ya kuma nanata goyon bayan kasar na samar da zaman lafiya a Sudan ta kudu tare da ganin an aiwatar da dukkan yarjejeniyoyin da kasashen biyu suka sanyawa hannu.

Al-Bashir ya ce, kundin ya shafi kowa da kowa kuma muryar al'ummar Sudan ce, kana kofa a bude take ga duk wadanda suka yi watsi da shirin a baya. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China