in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Sudan da Sudan ta Kudu sun amince da tsawaita yarjejeniyar cinikin man fetur
2016-12-21 09:43:23 cri
Kamfanin dillancin labarai na SUNA ya ruwato cewa, kasashen Sudan da Sudan ta Kudu, sun amince da tsawaita yarjejeniyar cinikin mai da suka rattabawa hannu a Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha wato Ethiopia a shekarar 2013.

Ministan man fetur da iskar gas na kasar Sudan Muhammad Zayed Awad, ya ce tun asali, yarjejeniyar ta shekaru uku ce, kuma a yanzu sun kara tsawaita ta zuwa wasu shekaru uku.

Ya yi bayanin cewa, kudin fitar da man Sudan ta Kudu ta iyakokin Sudan, zai ci gaba da kasancewa yadda yake, wato dala ashirin kan kowace gangar mai

Yayin da takwaransa na kasar Sudan ta Kudu, Ezekiel Gatkuoth a nasa bangare, ya bayyana jin dadi kan kara tsawaita yarjejeniyar da kasashen biyu suka cimma.

Ya kuma jadadda kudurin kasarsa na aiwatar da dukkan kunshin yarjejeniyar, yana mai cewa kasashen biyu sun amince su hada hannu kan batutuwan da suka shafi man fetur, tare da amfani da cibiyar horar da ma'aikatan mai wajen ba da horo, aiwaratar da bincike da kuma gwaje-gwaje.

Yarjejeniyar da kasar Sudan da Sudan ta Kudu suka cimma a watan Satumban 2012, ya yi tanadin cewa, Juba za ta bada dala biliyan uku ga Sudan a matsayin tallafi cikin shekaru uku, baya ga haka, gwamnatin Sudan ta Kudu za ta rika biyan kudin fitar da mai na dala ashirin kan kowace ganga. (Fa'iza)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China