in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya sun ce bidiyon da Boko haram ta fitar farfaganta ce
2016-12-30 19:22:02 cri
Rundunar sojojin najeriya ta bayyana faifan bidiyon da kungiyar Boko Haram ta fitar a matsayin farfagantar ta'addanci.

Wata sanarwa da kakakin sojojin Najeriyar Kanar Sani Usman ya rabawa manema labarai a yau Jumma'a, ya ce, sun kalli faifan bidiyon wanda jagoran kungiyar Abubakar Shekau ya fito yana wasu kalamai marasa tsuhe,kuma an dauki shi ne a wani wuri da ba a bayyana ba.

Abubakar Shekau dai ya fito a cikin bidiyon yanan karyata cewa, kungiyar tana nan daram a tungarta da ke dajin Sambisa

Sai dai kuma rundunar sojojin Najeriyar tana nanata cewa, ta kwace maboyar karshe ta makayan kungiyar da ke Dajin na Sambisa. Yanzu dai ana ci gaba da tantance sahihancin faifan bidiyon da kungiyar Boko Haram din ta fitar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China