in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe mambobin kwamitin sulhun MDD sun yi wata tattaunawar gaggawa a asirce kan batun Sham
2016-09-18 12:46:45 cri
A jiya Asabar, 17 ga wata ne, wakilan kasashe mambobin kwamitin sulhun MDD suka yi wata tattaunawar gaggauwa a asirce kan batun kawancen sojoji dake karkashin jagorancin kasar Amurka da ya jefa boma-bomai kan dakarun gwamnatin Sham a Deir ez-Zor dake gabashin kasar Sham. Wakilin kasar Rasha ya zargi kasar Amurka cewa, mai yiyuwa ne matakin da bangaren Amurka ya dauka zai gurgunta sabon shirin hadin gwiwar harkokin soja a tsakanin Rasha da Amurka kan batun Sham da ya kamata ya fara aiki a ranar Litinin, 19 ga wata.

Kwamitin sulhun ya shirya wannan tattaunawar ce bisa bukatar da Rasha ta gabatar. Kafin ta shiga dakin tattaunawar, madam Samantha Power ta gaya wa 'yan jarida cewa, bangaren Amurka ya dauka cewa, an jefa boma-bomai ne kan na'urorin kungiyar IS, bayan da bangaren Rasha ya sanar da cewa, kayayyakin da aka kai hari, kayayyakin dakarun gwamnatin Sham ne, sai dai kawancen sojojin dake karkashin kasar Amurka ya daina jefa boma-boman, yanzu bangaren Amurka yana binciken lamarin. Idan aka tabbatar da cewa, kayayyakin dakarun gwamnatin Sham ne aka kaiwa wannan hari, to, ana iya cewa, wannan wani kuskure ne. Kuma Amurka ba ta jefa boma-boman da ganga ba. Ta kuma ce, kasar Rasha ta gangan ta kira wannan taron tattaunawar gaggawa.

Bayan kammala taron, Mr. Vitaly Churkin, wakilin dindindin na kasar Rasha dake MDD ya gaya wa 'yan jarida cewa, kasar Rasha za ta zuba ido kan martanin kasar Amurka, tana kuma fatan Amurka za ta mai da hankali sosai kan yadda za a daidaita batun Sham a siyasance. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China