in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha za ta dauki mataki kan sabon takunkumin da Amurka ta sanya mata
2016-12-30 10:03:01 cri
Sakataren watsa labarai na shugaban kasar Rasha Dmitri Peskov, ya bayyana a jiya Alhamis cewa, Rasha za ta dauki matakai kan sabon takunkumin da kasar Amurka ta kakaba mata.

Dmitri Peskov ya ce, kasarsa za ta tsara matakai bisa umurnin shugaba Vladimir Putin, domin mai da martani kan takunkumin da Amurka ta sanya mata.

A cewarsa, wannan takunkumin da Barack Obama ya sanyawa Rasha, zai lalata dangantakar dake tsakanin Rasha da Amurka, kana ya kawo illa ga manufar diflomasiyya da zababben shugaban kasar wato Donald Trump, ya tsara.

Peskov ya kuma ce, gwamnatin Obama na kokarin matsawa gwamnatin Trump lamba ta hanyar nuna kiyayya ga kasar ta Rasha.

Mista Peskov ya kara da cewa, gwamnatin Rasha tana fatan gwamnatin Obama za ta gyara matakanta, ta yadda huldar dake tsakanin kasashen biyu za ta bunkasa ta hanyar da ta dace.

Jiya Alhamis 29 ga wata, shugaban kasar Amurka mai barin gado Barack Obama ya sanar da cewa, kasarsa za ta sanyawa Rasha takunkumi, bisa zarginta da yin katsalandan cikin harkokin zaben Amurka ta yanar gizo wato Intanet.

Har ila yau, a jiya Alhamis din ne, ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta sanar da korar 'yan diflomasiyyar Rasha 35 daga kasar. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China