in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Tanzaniya na barazanar fadawa cikin Hamada
2016-05-03 11:33:48 cri
Ministan kula da muhalli na kasar Tanzaniya January Makamba ya bayyana cewa, muddin mahukuntan kasar ba su dauki matakan da suka wajaba ba, babu makawa kashi 61 cikin 100 na yankunan kasar na cikin barazanar zama hamada.

Makamba wanda ya bayyana hakan ga majalisar dokokin kasar da ke birnin Dodoma, ya ce kasar tana hasarar abin da ya kai eka miliyan daya na dazuka a kowace shekara. Yana mai cewa, a cikin shekaru 10 da suka gabata kadai kasar ta rasa yankin da ya kai kwatankwacin fadin kasar Rwanda.

Ministan ya ce, babban abin da ke haddasa wannan matsala ita ce, yadda jama'a ke sare itatuwa domin neman makamashi. Kuma yanzu haka kasar ta fara dandana illar matsalar yanayi, inda ake samun kanfon ruwan sama da karuwar zafi.

Jami'in ya ce, yanzu haka gwamnati ta kaddamar da shirin dasa itatuwa a fadin kasar domin kawar da wannan matsala, inda take sa ran dasa itatuwa miliyan 1.5 a kowace shekara, baya ga samarwa hukumar kare muhalli ta kasar (NEMC) kudi da kayan aiki domin ta yaki duk wasu abubuwan da ke kawo illa ga muhalli. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China