in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Al'ummar kasar Zimbabwe na gudanar da bikin Kirisimeti cikin rashin isassun kudade
2016-12-27 09:58:09 cri
Yayin da ake bikin Kirisimeti da na shiga sabuwar shekara, rahotanni sun bayyana cewa, al'ummar kasar Zimbabwe na fuskantar matsalar rashin kudi.

Ma'aikatan gwamnati ne dai suka fi shiga cikin tasku, domin galibinsu, ba za su samu albashinsu ba, har sai bayan an kare hutu da za a yi cikin watan nan na Disamba.

Ma'aikatan lafiya da masu kayan sarki ne kadai, suka samu albashi kafin ranar Kirisimetin a ranar 21 ga watan nan, yayin da za a biya malamai a gobe, 28 ga wata, inda sauran kuma sai a ranar 3 ga watan Junairun sabuwar shekara.

Kamar kullum, 'yan fansho su ne a karshe, inda za a biya su a ranar 6 ga watan Junairun 2017, bayan an kammala bukukuwan.

Duk da ma'aikatan gwamnati ba sa farin ciki da wannan al'amari, gwamnatin ta tsinci kanta cikin matsalar rashin kudi, inda a kowanne wata take fafutukar biyan albashin dake lakume sama da kashi casa'in na kudin shigar kasar.

Ko a bara, hakan ce ta kasance, domin kuwa gwamnati ba ta biya ma'aikata ba sai bayan an kammala bukukuwan. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China