in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta taimakawa kasar Zimbabwe wajen rage yawan mutane da suka kamu da ciwon sankarar mahaifa
2016-12-16 13:28:31 cri

A matsayin daya daga cikin ayyukan kiwon lafiyar mata da yara guda 100 a kasashe masu tasowa da kasar Sin take gudanar, an kaddama da aikin bada jinya ga mutanen da suka kamu da ciwon sankarar mahaifa da kasar Sin ta gudanar a asibitin Parirenyatwa dake birnin Harare na kasar Zimbabwe. Za dai a shafe makwani biyu ana aikin jinya, da mu'amalar fasahohi, da sauransu a fannin yaki da ciwon sankara a mahaifa.

A gun bikin kaddamar da aikin, Sin ta bada na'urorin kyauta ga asibitin Parirenyatwa, kayayyakin da darajarsu ta kai dala dubu 500, don samun nasarar jinya da magance ciwon sankarar mahaifa a kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China