in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mugabe ya ce masu neman sauya gwamnatin Zimbabwe ba za su yi nasara ba
2016-12-17 12:35:50 cri
Shugaba Robert Mugabe na kasar Zimbabwe ya sanar a jiya Juma'a cewa, masu yunkurin sauya shugabancin kasar ba za su kai ga nasara ba, kana ya bukaci magoya bayan jam'iyyarsa da su hada kai domin ciyar da kasar gaba.

Da yake jawabi ga taron shekara-shekara na magoya bayan jam'iyyar ta Zanu-PF a tsakiyar garin Masvingo, Mugabe, wanda shi ne sakataren jam'iyyar na farko, ya bayyana cewa jam'iyyar Zanu PF tana nan daram duk kuwa da irin makircin da ya ce 'yan adawar kasar, da kuma makiyan kasashen yammacin duniya suke nunawa gwamnatinsa.

Mugabe ya ce "jam'iyyarmu ta kasance mai karfi. Ba na tantama game da haka. Kasashen da suke nuna mana kiyayya, sun dauki tsawon lokaci suna kokarin ganin bayan wannan gwamnati, amma ba za su samu nasarar canza wannan shugabanci ba". (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China