in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Harin kunar bakin wake ya hallaka mutane biyu a jamhuriyar Kamaru
2016-12-26 10:11:16 cri
A Jiya Lahadi 25 ga wata, wani harin kunar bakin wake da aka kaddamar a garin Mora dake yankin arewa mai Nisa a jamhuriyar Kamaru, ya yi sanadiyyar mutuwar mutane biyu.

Wata majiya daga rundunar sojan kasar ta Kamaru ta ce, an kai harin ne da misalin karfe 8 na safiyar agogon kasar, inda 'yan kunar bakin waken biyu suka tayar da boma bomai dake jikinsu a kofar shiga wata kasuwa dake garin Mora.

Sai dai baya ga mutuwar 'yan kunar bakin waken biyu, kawo yanzu ba'a samu rahoton mutuwa ko jikkatar ko da mutum guda ba.

Ana zargin wadannan 'yan kunar bakin waken biyu dakaru ne na kungiyar Boko Haram.

A watan Faburairun shekara ta 2015, a birnin Yaounde na jamhuriyar Kamaru, membobi na kwamitin kasashen dake gabar tafkin Chadi gami da kasar Benin, suka sanar da kafa rundunar hadin gwiwa mai kunshe da sojoji sama da 8700, da zummar murkushe kungiyar Boko Haram. A garin Mora ma an jibge sojojin kasashe daban-daban. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China