Harin ya faru ne da misalin karfe 7 na safe a garin Mora, wanda ke yankin arewa mai nisa a jamhuriyar Kamara mai makwabtaka da Najeriya, ana zargin wasu mata biyu 'yan kungiyar Boko Haram ne suka kaddamar da harin.
An kashe daya daga daga cikin maharan ne, a dai dai lokacin da ta yi yunkurin kutsawa kasuwa garin Mora. Kana harin na biyu ya hallaka 'yar kunar bakin waken da kuma raunata fararen hula biyu.
Sai dai har yanzu ba'a sanar da harin ba a hukumance.(Ahmad Fagam)