in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Najeriya za ta biya lada ga wadanda suka tona asirin barayin gwamnati
2016-12-22 09:36:51 cri
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta amince da wani shiri na biyan lada ga wadanda suka tona asirin barayin gwamnatin, a wani mataki na karfafa shirin gwamnati na yaki da cin hanci da rashawa.

Ministar kudin kasar Femi Adeosun ce ta bayyana hakan ga taron manema labarai a Abuja, fadar mulkin kasar, bayan da taron majalisar zartarwar kasar wanda shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranta ya amince da shirin.

Karkashin shirin gwamnati za ta baiwa duk wanda ya fallasa asirin barayin gwamnati ladan kaso biyar cikin 100 na kudaden da aka gano. Haka kuma gwamnati za ta dauki matakan da suka wajaba don an kare wadanda suka fassala barayin daga duk wani abu da ka iya samunsu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China