in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya ya ce ba a shigar da kowa da kowa cikin harkokin ci gaban da duniya ke samu
2016-12-21 09:21:10 cri
A cikin wata sanarwar da ya fitar, sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon, ya ce ba a shigar da kowa da kowa cikin batutuwan ci gaban da duniya ta samu, yana mai cewa akwai bukatar samun hadin kai da kaunar juna wajen cike gibin dake akwai na samar da ci gaba a duniya.

A wani bangare na bikin ranar hadin kai da mara baya ga juna ta duniya da ake yi yau, Ban Ki-moon, ya bayyana rashin samar da daidaito da rashin aikin yi da gurbatar muhalli a matsayin muhimman batutuwa ga al'ummomin duniya.

Ya ce a lokacin da ake samun rarrabuwar kawuna a kan batutuwa da dama da suka hada da matsalar kungiyoyin 'yan ta'adda da ta gudun hijra bisa tilas, akwai bukatar mutane su mara baya ga juna wajen cimma muradin da suka sanya gaba, maimakon gujewa juna saboda tsaro.

Ya kuma bukaci kasashen duniya su tabbatar da shigar da al'umma cikin harkokin raya kasa tare da tabbatar da daidaito, ta hanyar aiwaratar da munufofin muradu masu dorewa, da kuma yarjejeniyar yanayi da aka cimma a birnin Paris, da nufin gina ingantacciyar rayuwa ga kowa.

Ana bikin wannan rana ta hadin kai da mara baya ga juna ne a duk 20 ga watan Disamban kowace shekara. Kuma ranar a bana na kira ne da aiwatar da muradun nan goma sha bakwai masu dorewa da nufin yaki da fatara, kare ban kasa, tare da kare mutuncin kowa. (Fa'iza)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China