Shugaba Erdogan ya bayyana kisan jakadan a matsayin takalar fada da nufin lalata dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.
Erdogan ya ce, ya tattauna da takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin, inda ya ba da umarnin tura jami'an tsaron kasar Turkiya don su gudanar da bincike game da lamarin.
Rahotanni na cewa, wani dan bindiga ne sanye da bakar kwat da laktaya ya harbe jakadan kasar ta Rasha da ke Turkiya lokacin da ya ke jawabi a bikin bude kolin zane-zane a birnin Ankara.
Kafofin tsaron Turkiya sun bayyana cewa, dan bindigar yana kabbara da kururuwar cewa, kar ku manta da Aleppo da Syria da 'yan uwanmu, kana daga bisi ya bude wuta.
Ministan harkokin cikin gidan na kasar Turkiya Suleyman Soylu, ya bayyana cewa, an harbe dan bindigar mai shekaru 22 da haihuwa har lahari a wurin da lamarin da faru. An kuma gano cewa, dan bindigar jami'in dan sandan Turkiya ne mai Mevlut Mert Altintas. (Ibrahim Yaya)