A daren jiya Litinin ne, shugaban kasar Rasha Putin ya yi Allah wadai da kakkausar murya dangane da kisan da aka yi wa jakadan kasarsa dake kasar Turkiya. Shugaba Putin ya jaddada cewa, zai kara daukar matakan yaki da ta'addanci domin hana sake aukuwar wannan lamari.
A wannan rana, kakakin ma'aikatar harkokin wajen Rasha Maria Zakharowa ta bayyana cewa, kisan jakadan Rasha dake Turkiya tamkar harin ta'addanci ne, kuma Rasha za ta gabatar da batun ga kwamitin sulhun MDD domin ya gudanar da bincike.(Jamila)