in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MPP ta zargi masu ta'awar jihadi da kaddamar da hari kan bari Soja a Burkina Faso
2016-12-19 10:03:27 cri
Jam'iyyar MPP mai mulki a kasar Burkina-Faso ta zargi wasu gungun masu da'awar jiha da hannu a mummunan harin da aka kaddamar ranar Jumma'a kan wani sansanin sojoji da ke kusa da iyakar kasar Mali.

Rahotanni na cewa, kimanin wasu 'yan bindiga dauke da makamai da ba a tantance su guda 40 ne suka kai hari a kan sansanin sojojin na Nassoumbou, inda suka hallaka sojoji 12.

A cikin wata sanarwar da jam'iyyar MPP ta rabawa manema labarai a ranar Asabar, ta yi Allah-wadai da kakkausar murya kan abin da kira harin dabbaci da aka kai, kana ta jinjinawa sojojin da aka kashe a yayin da suke kokarin kare martabar kasarsu.

Bugu da kari, jam'iyyar ta yi Allah-wadai da matakan 'yan ta'addan na kokarin jefa kasar cikin tashin hankali. A don haka ta bukaci gwamnati da ta kara sanya ido don gudun aukuwar irin wadannan hare-hare a nan gaba.

Kasar Burkian-Faso dai ta fuskanci tashe-tashen hankulan a wannan shekara da ke shirin karewa ta 2016, inda a watan Janairu wasu 'yan bindiga suka kaddamar da munanan hare-hare a dakin cin abincin Cappuccino da otel din Splendid a Ouagadougou, babban birnin kasar, hare-haren da suka yi sanadiyar rayukan mutane 30. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China